Hausa
Surah Al-Qamar ( The Moon ) - Aya count 55
اقْتَرَبَتِ السَّاعَةُ وَانشَقَّ الْقَمَرُ
( 1 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 1 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 1](style/islamic/icons/mp3.png)
Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.
وَإِن يَرَوْا آيَةً يُعْرِضُوا وَيَقُولُوا سِحْرٌ مُّسْتَمِرٌّ
( 2 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 2 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 2](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"
وَكَذَّبُوا وَاتَّبَعُوا أَهْوَاءَهُمْ ۚ وَكُلُّ أَمْرٍ مُّسْتَقِرٌّ
( 3 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 3 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 3](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.
وَلَقَدْ جَاءَهُم مِّنَ الْأَنبَاءِ مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌ
( 4 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 4 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 4](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.
حِكْمَةٌ بَالِغَةٌ ۖ فَمَا تُغْنِ النُّذُرُ
( 5 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 5 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 5](style/islamic/icons/mp3.png)
Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ ۘ يَوْمَ يَدْعُ الدَّاعِ إِلَىٰ شَيْءٍ نُّكُرٍ
( 6 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 6 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 6](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.
خُشَّعًا أَبْصَارُهُمْ يَخْرُجُونَ مِنَ الْأَجْدَاثِ كَأَنَّهُمْ جَرَادٌ مُّنتَشِرٌ
( 7 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 7 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 7](style/islamic/icons/mp3.png)
¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.
مُّهْطِعِينَ إِلَى الدَّاعِ ۖ يَقُولُ الْكَافِرُونَ هَٰذَا يَوْمٌ عَسِرٌ
( 8 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 8 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 8](style/islamic/icons/mp3.png)
Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"
كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍ فَكَذَّبُوا عَبْدَنَا وَقَالُوا مَجْنُونٌ وَازْدُجِرَ
( 9 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 9 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 9](style/islamic/icons/mp3.png)
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.
فَدَعَا رَبَّهُ أَنِّي مَغْلُوبٌ فَانتَصِرْ
( 10 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 10 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 10](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."
فَفَتَحْنَا أَبْوَابَ السَّمَاءِ بِمَاءٍ مُّنْهَمِرٍ
( 11 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 11 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 11](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.
وَفَجَّرْنَا الْأَرْضَ عُيُونًا فَالْتَقَى الْمَاءُ عَلَىٰ أَمْرٍ قَدْ قُدِرَ
( 12 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 12 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 12](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.
وَحَمَلْنَاهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلْوَاحٍ وَدُسُرٍ
( 13 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 13 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 13](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.
تَجْرِي بِأَعْيُنِنَا جَزَاءً لِّمَن كَانَ كُفِرَ
( 14 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 14 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 14](style/islamic/icons/mp3.png)
Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.
وَلَقَد تَّرَكْنَاهَا آيَةً فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ
( 15 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 15 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 15](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
( 16 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 16 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 16](style/islamic/icons/mp3.png)
To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ
( 17 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 17 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 17](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ عَادٌ فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
( 18 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 18 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 18](style/islamic/icons/mp3.png)
Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?
إِنَّا أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رِيحًا صَرْصَرًا فِي يَوْمِ نَحْسٍ مُّسْتَمِرٍّ
( 19 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 19 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 19](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.
تَنزِعُ النَّاسَ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ مُّنقَعِرٍ
( 20 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 20 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 20](style/islamic/icons/mp3.png)
Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
( 21 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 21 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 21](style/islamic/icons/mp3.png)
To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ
( 22 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 22 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 22](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِالنُّذُرِ
( 23 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 23 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 23](style/islamic/icons/mp3.png)
Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.
فَقَالُوا أَبَشَرًا مِّنَّا وَاحِدًا نَّتَّبِعُهُ إِنَّا إِذًا لَّفِي ضَلَالٍ وَسُعُرٍ
( 24 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 24 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 24](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.
أَأُلْقِيَ الذِّكْرُ عَلَيْهِ مِن بَيْنِنَا بَلْ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٌ
( 25 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 25 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 25](style/islamic/icons/mp3.png)
"Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"
سَيَعْلَمُونَ غَدًا مَّنِ الْكَذَّابُ الْأَشِرُ
( 26 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 26 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 26](style/islamic/icons/mp3.png)
Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?
إِنَّا مُرْسِلُو النَّاقَةِ فِتْنَةً لَّهُمْ فَارْتَقِبْهُمْ وَاصْطَبِرْ
( 27 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 27 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 27](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.
وَنَبِّئْهُمْ أَنَّ الْمَاءَ قِسْمَةٌ بَيْنَهُمْ ۖ كُلُّ شِرْبٍ مُّحْتَضَرٌ
( 28 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 28 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 28](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.
فَنَادَوْا صَاحِبَهُمْ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ
( 29 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 29 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 29](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
( 30 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 30 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 30](style/islamic/icons/mp3.png)
To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?
إِنَّا أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ صَيْحَةً وَاحِدَةً فَكَانُوا كَهَشِيمِ الْمُحْتَظِرِ
( 31 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 31 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 31](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ
( 32 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 32 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 32](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ بِالنُّذُرِ
( 33 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 33 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 33](style/islamic/icons/mp3.png)
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.
إِنَّا أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ حَاصِبًا إِلَّا آلَ لُوطٍ ۖ نَّجَّيْنَاهُم بِسَحَرٍ
( 34 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 34 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 34](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.
نِّعْمَةً مِّنْ عِندِنَا ۚ كَذَٰلِكَ نَجْزِي مَن شَكَرَ
( 35 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 35 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 35](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.
وَلَقَدْ أَنذَرَهُم بَطْشَتَنَا فَتَمَارَوْا بِالنُّذُرِ
( 36 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 36 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 36](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.
وَلَقَدْ رَاوَدُوهُ عَن ضَيْفِهِ فَطَمَسْنَا أَعْيُنَهُمْ فَذُوقُوا عَذَابِي وَنُذُرِ
( 37 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 37 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 37](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."
وَلَقَدْ صَبَّحَهُم بُكْرَةً عَذَابٌ مُّسْتَقِرٌّ
( 38 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 38 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 38](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.
فَذُوقُوا عَذَابِي وَنُذُرِ
( 39 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 39 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 39](style/islamic/icons/mp3.png)
To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ
( 40 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 40 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 40](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
وَلَقَدْ جَاءَ آلَ فِرْعَوْنَ النُّذُرُ
( 41 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 41 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 41](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.
كَذَّبُوا بِآيَاتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذْنَاهُمْ أَخْذَ عَزِيزٍ مُّقْتَدِرٍ
( 42 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 42 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 42](style/islamic/icons/mp3.png)
Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.
أَكُفَّارُكُمْ خَيْرٌ مِّنْ أُولَٰئِكُمْ أَمْ لَكُم بَرَاءَةٌ فِي الزُّبُرِ
( 43 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 43 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 43](style/islamic/icons/mp3.png)
Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?
أَمْ يَقُولُونَ نَحْنُ جَمِيعٌ مُّنتَصِرٌ
( 44 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 44 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 44](style/islamic/icons/mp3.png)
Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"
سَيُهْزَمُ الْجَمْعُ وَيُوَلُّونَ الدُّبُرَ
( 45 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 45 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 45](style/islamic/icons/mp3.png)
Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.
بَلِ السَّاعَةُ مَوْعِدُهُمْ وَالسَّاعَةُ أَدْهَىٰ وَأَمَرُّ
( 46 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 46 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 46](style/islamic/icons/mp3.png)
Ã'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.
إِنَّ الْمُجْرِمِينَ فِي ضَلَالٍ وَسُعُرٍ
( 47 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 47 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 47](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.
يَوْمَ يُسْحَبُونَ فِي النَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمْ ذُوقُوا مَسَّ سَقَرَ
( 48 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 48 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 48](style/islamic/icons/mp3.png)
Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."
إِنَّا كُلَّ شَيْءٍ خَلَقْنَاهُ بِقَدَرٍ
( 49 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 49 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 49](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.
وَمَا أَمْرُنَا إِلَّا وَاحِدَةٌ كَلَمْحٍ بِالْبَصَرِ
( 50 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 50 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 50](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.
وَلَقَدْ أَهْلَكْنَا أَشْيَاعَكُمْ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ
( 51 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 51 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 51](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?
وَكُلُّ شَيْءٍ فَعَلُوهُ فِي الزُّبُرِ
( 52 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 52 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 52](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.
وَكُلُّ صَغِيرٍ وَكَبِيرٍ مُّسْتَطَرٌ
( 53 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 53 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 53](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَنَهَرٍ
( 54 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 54 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 54](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.
فِي مَقْعَدِ صِدْقٍ عِندَ مَلِيكٍ مُّقْتَدِرٍ
( 55 ) ![Hausa - Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 55 Al-Qamar ( The Moon ) - Aya 55](style/islamic/icons/mp3.png)
A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.